Ƴan tawaye sun kashe sojojin wanzar da zaman lafiya 13 Jamhuriyar Congo



An kashe sojojin wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya guda 13 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo sanadiyyar tashin hankalin da ake fama da shi a ƙasar.


Rundunar sojin Afirka ta Kudu wadda dakarunta ke cikin masu ƙoƙarin wanzar da zaman lafiyar a Congo ta ce an kashe sojojinta guda 9 a lokacin da ake fafutikar hana mayaƙan ƴan tawaye na ƙungiyar M23 daga dannawa zuwa birnin Goma da ke gabashin ƙasar ta Congo.


Haka nan daga cikin waɗanda aka kashen akwai sojojin Malawi guda uku da kuma na Uruguay guda ɗaya.


Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ya ce ya yi magana da shugabannin ƙasashen na Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo da kuma na Rwanda yayin da ake ci gaba da kira da kawo ƙarshen rikicin.

Comments

Popular Posts